in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Sama da mutane 40 ne zaftarewar laka ta yi sanadiyyar mutuwarsu a arewa maso gabashin Jamhuriyar Demokradiyyar Congo
2017-08-18 10:27:59 cri
Wata majiya dake da kusanci da gwamnan Lardin Ituri na Jamhuriyar Demokradiyyar Congo, ta ce sama da mutane 40 ne suka mutu yayin da wasu sama da 100 suka bata, sanadiyyar zaftarewar laka da ta auku jiya Alhamis a kauyen Tora dake kusa da tafkin Albert na lardin Ituri.

Wani dan kungiyar al'umma Mugisa Mbogemu, ya ce zaftarewar lakar ta auku ne a kauyen Tora dake kusa da tafkin Albert, bayan mamakon ruwan sama da aka shafe ana yi da daren ranar.

Mugisa Mbogemu dake kauyen Tchomia wanda ke makotaka da inda iftil'in ya auku, ya ce yanzu haka lakar ta binne kauyen, kuma ana kokarin ceto mutane.

A cewar wani likita dake yankin Tchomia, kawo yanzu daruruwan mutane ne ke binne karkashin lakar, yayin da aka garzaya da wasu da aka ceto ciki har da mata da yara zuwa asibiti mafi kusa .

Kauyen da iftila'in ya auku na kusa ne da tafkin Albert.

Ana ta samun rahotannin zaftarewar laka a wasu kauyuka, galibi wadanda ke tsakanin tabkuna ko tsaunuka. (Fa'iza Mustapha)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China