Yau Alhamis, rana ce ta karshe da mai martaba sarkin Kano, Muhammadu Sanusi II, da 'yan tawagarsa suka yi ziyarar aiki kasar Sin, inda da safe suka ziyarci ofishin asusun raya nahiyar Afirka na kasar Sin, wato China-Africa Development Fund. Babban manajan asusun, Mista Chi Jianxin da mai martaba sarkin Kano sun yi musanyar ra'ayi, game da yadda za su karfafa hadin-gwiwa da mu'amala ta fuskar cinikayya da zuba jari.(Murtala Zhang)