in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Kasar Saliyo na cikin matsananciyar bukatar agaji bayan annobar zaftarewar laka da ta auku
2017-08-17 09:58:56 cri
Kakakin fadar Shugaban kasar Saliyo Abdulai Bayraytay, ya ce kasar na tsananin bukatar abinci da ruwa da tufafi da matsugunai, da magunguna, ga dubban mutanen da ambaliyar zaftarewar laka da ta auku a wani gari dake kusa da birnin Freetown a ranar Litinin, ta raba da muhallansu.

Abdulai Bayraytay, wanda kuma shi ne babban jami'in aikin tunkarar annoba a Saliyo, ya shaidawa kamfanin dillancin labarai na Xinhua cewa, sun samar da wajen zama na wucin gadi ga wadanda suka rasa muhallansu a makarantu daban-daban dake birnin, kuma a yanzu haka, suna samar da busassashen abinci ga mutanen, sai dai duk da haka suna bukatar kari.

Ya kara da cewa yayin da ake bukatar wadancan abubuwa, har yanzu ana ci gaba da aikin gano wadanda ake tsammanin lakar ta binne su.

Jami'in ya ce gwamnati ta damu game da yuwar barkewar cutar amai da gudawa bayan annobar, a don haka take tsananin bukatar magunguna.

Wata sanarwa daga fadar shugaban kasar da aka fitar ranar Talata, ta ce mata 83 da maza 105 da kuma yara 109 ne suka mutu sanadiyyar annobar. Sannan yayin da ake ci gaba da aikin ceto, mai yuwa ne a samu karin gawarwaki.

Sanarwar ta ce ana kai gawawwakin ne asibitin Connaught dake birnin Freetown. (Fa'iza Mustapha)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China