in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Kamfanonin kasar Sin sun baiwa Saliyo gudumawar dala 200,000 sakamakon bala'in da ya auka mata
2017-08-17 09:14:27 cri
A jiya Laraba ne, kamfanonin kasar Sin da tawagar ma'aikatan lafiya dake aiki a kasar Saliyo suka bayar da gudumawar tsabar kudi har dala 200,000 gami da wasu kayayyaki, don taimakawa kokarin gwamnatin kasar na agaza wadanda bala'in ambaliyar ruwa da zaftarewar laka ta shafa.

Da yake jawabi yayin bikin mika kayayyakin, jami'in diflomasiyar kasar Sin dake kasar ta Saliyo Wang Xinmin, ya bayyana cewa, al'ummar kasar Sin suna tare da takwarorinsu na Saliyo a wannan lokaci na bakin ciki, kasancewar kasashen biyu tamkar Danjuma ne da Danjummai.

Ya ce yanzu haka, gwamnatin kasar Sin tana kokarin turo da nata tallafin, ta yadda gwamnatin Saliyo za ta taimakawa wadanda wannan bala'in ya shafa.

A nasa jawabin, mataimakin shugaban kasar Saliyo Victor Bockarie Foh, ya yaba da wannan taimako na kamfanonin kasar Sin dake zauna a kasar ta Saliyo. Ya kuma ba da tabbacin cewa, za a yi amfani da kudade da kayayyakin da aka samar ta hanyar da ta dace.

Ya kuma bayyana matakan da gwamnatin Saliyon ke dauka na ganin an kwashe wadanda ke zaune a yankunan da ake fuskantar barazanar ambaliyar zuwa yankuna marasa hadari, tare kuma da gina musu gidaje masu saukin kudi.

Iftila'in na ranar Litinin da ya rutsa da wajen birnin Freetown, babban birnin kasar, ya binne daruruwan mutane a unguwanni da dama, ciki har da Regent, tsaunin Sugar-Loaf, Kamayama, Kaningo da Dworzark da sauransu.

Wannan dai shi ne bala'in mafi muni da ya taba aukuwa a kasar a tarihinta, inda bayanai ke nuna cewa, dubban mutane sun rasa matsugunansu a sassan birnin Freetown. (Ibrahim Yaya)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China