Sin: Bai kamata a yi amfani da batun addini wajen tsoma baki kan harkokin cikin gidan sauran kasashe ba
A yau Laraba ne, a nan birnin Beijing, fadar mulkin kasar Sin, kakakin ma'aikatar harkokin wajen kasar Madam Hua Chunying ta bayyana cewa, rahoton da kasar Amurka ta gabatar wanda ke korafe-korafe kan yanayin 'yancin bin addini a kasar Sin ba gaskiya ba ne,don haka kasar Sin ta kalubalanci kasar Amurka da ta girmama hakikanin halin da ake ciki, ta kuma kula da harkokin dake gabanta, kana ta daina amfani da batun addini tana tsoma baki a harkokin cikin gidan sauran kasashe. (Zainab)
Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku