A jiya Talata ne,Mai martaba sarkin Kano Muhammadu Sanusi II ya iso nan birnin Beijing, domin ci gaba da ziyarar da yake a kasar Sin. Daga nan dakin mu na watsa shirye-shirye na tambayi wakilinmu Murtala Zhang wanda yake tare da tawagar sarkin game da wuraren da sarkin na Kano zai ziyarta a nan birnin Beijing.