in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Ana fatan kasar Japan za ta duba hakikanin tarihi na kai hari ga kasar Sin
2017-08-15 20:23:04 cri
Yau Talata 15 ga watan Agusta ce ranar cika shekaru 72, tun bayan da harin da kasar Japan ta kaiwa Sin ya ci tura wanda hakan ya sanya ta ajiye makamai.

A wannan rana a nan birnin Beijing, kakakin ma'aikatar harkokin wajen kasar Sin Hua Chunying ta bayyana cewa, a yayin yakin duniya na biyu, sojojin kasar Japan sun kai hari mai tsanani ga jama'ar kasar Sin. Akwai shaidu a tarihi, wadanda ba za a iya musanta su ba. Kuma Sin tana fatan kasar Japan za ta duba hakikanin tarihi game da harin ta kan kasar Sin, ta girmama jama'ar kasashen Asiya ciki har da kasar Sin, wadanda suka sha fama sakamakon hare haren mayakan kasar ta Japan. (Zainab)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China