in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Ya kamata a karfafa hadin gwiwa tsakanin kafofin watsa labarai na Sin da Afirka
2017-08-15 11:02:32 cri

A jiya Litinin, an yi wani taron musayar ra'ayi tsakanin kafofin watsa labaru na kasashen Afirka da na kasar Sin a birnin Johannesburg na kasar Afirka ta Kudu. Masu halartar taron sun hada da mataimakin babban daraktan ofishin watsa labaru na majalisar gudanarwar kasar Sin Guo Weimin, da jakadan kasar Sin dake Afirka ta Kudu Lin Songtian, da wakilan kafofin watsa labarun kasar Sin dake Afirka ta Kudu, da kuma wakilan kafofin watsa labaru 15 na kasashe daban daban dake nahiyar Afirka.

Cikin jawabin da ya gabatar wajen taron, mista Guo Weimin ya ce,

"Akwai karancin fahimtar juna tsakanin bangarorin Sin da Afirka, idan aka kwatanta da ci gaban da aka samu a fanin hadin gwiwar bangarorin 2. Saboda haka ya ba da shawarar kara yin hadin kai, tsakanin kafofin watsa labaru na bangarorin 2, domin tabbatar da samar da murya mai adalci da sanin ya kamata. "

Dangane da yadda za a zurfafa hadin gwiwa a tsakanin kafofin yada labaru na Sin da Afirka, mista Guo Weimin ya ce,

"Ya kamata a karfafa fahimtar juna tsakanin kafofin watsa labarai na kasar Sin da na kasashen Afirka, tare da karfafa hadin gwiwar dake tsakaninsu, domin daukaka mu'amalar bangarorin biyu zuwa wani sabon matsayi. Sannan kuma, bangarorin biyu su bayyana ra'ayoyinsu yadda ya kamata a duniya bisa hadin gwiwa da mu'amalar dake tsakaninsu."

A nasa bangare Timothy Olariwaju, babban editan jaridar' the Sun' ta kasar Najeriya, cewa ya yi

"har yanzu a Najeriya, mutane da yawa suna sauraron labarai ta hanyar rediyo. Kuma bisa kafa sashen Hausa da gidan rediyon kasar Sin ya yi, ya sa 'yan Najeriya jin dadin sauraron bayanan da ake watsa wa ta harshen Hausa, wadanda suka shafi al'adun kasar Sin, da ayyukan gini da Sinawa suke yi a Najeriya. kokarin da CRI ke yi wajen watsa labarai ga kasashen Afirka yana tare da nasarori, ya kuma yi fatan ganin gidan rediyon ya fara watsa labarai ga karin kasashen dake nahiyar Afirka."

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China