Ambaliyar ruwa da zaizayar kasa sun haddasa mutuwar mutane kimanin 200 a Saliyo
An yi ruwan sama kamar da bakin kwarya a birnin Freetown hedkwatar kasar Saliyo a yau Litinin, lamarin da ya haddasa ambaliyar ruwa da zaizayar kasa. An ce mutane kimanin 200 ne suka rasa rayukansu sakamakon aukuwar wannan bala'i. Tuni kuma mahukuntan kasar suka bayyana cewa, an riga an jibge sojoji don taimakawa wajen aikin ceton al'umma. (Bello Wang)
Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku