in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Sin ta jaddada adawar ta ga manufofin Dalai Lama
2017-08-14 19:48:38 cri
Mai magana da yawun ma'aikatar wajen kasar Sin Hua Chunying, ta jaddada aniyar kasar Sin na adawa da ayyukan raba kawuna, da dan awaren nan dan asalin kasar ta Sin Dalai Lama ke aikatawa, duk kuwa da soke ziyarar da Dalai Laman ya yi zuwa kasar Botswana.

Rahotanni sun bayyana cewa, Dalai Lama ya soke tafiyar da ya shirya zuwa Botswana ne a tsakiyar watan nan na Agusta, bisa dalilai na rashin lafiya.

Da take tsokaci game da hakan, Hua Chunying ta ce Sin na daukar alakar kawancen ta da Botswana da matukar muhimmanci, tana kuma fatan hakan zai dore, ya kuma kai ga haifar da ci gaba mai dorewa tsakanin sassan biyu. (Saminu Alhassan)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China