Jiya Lahadi ne, mai martaba sarkin Kano, Muhammadu Sanusi II ya iso nan birnin Shanghai dake gabashin kasar Sin, domin ci gaba da ziyarar aikin da ya ke yi a kasar Sin. Wannan shi ne karo na farko da sarkin na Kano ya zo birnin Shanghai, wanda shi ne cibiyar kasuwanci da tattalin arziki ta kasar ta Sin. Wakilinmu Murtala Zhang ya samu damar zantawa da mai martaban, bayan da ya ziyarci babban dakin nuna yadda aka tsara fasalin birnin Shanghai. Ga cikakkaiyar hirarsu.
Wakilinmu Murtala Zhang ke nan a zantawarsa da mai martaba sarkin Kano Muhammadu sanusi na biyu a birnin Shanghai. Yau Litinin kuma, mai martaba sarkin Kano Muhammadu Sanusi II da 'yan tawagarsa za su ci gaba da ziyarar da suke a birnin Shanghai, inda wakilinmu Murtala zai aiko mana rahotanni game da wannan ziyara.
Da fatan za ku kasance tare da mu.