Jiya Asabar da safe, mai martaba sarkin Kano Muhammadu Sanusi II, wanda a yanzu haka yake ziyarar aiki kasar Sin, ya ziyarci babban dakin adana kayan tarihi na birnin Shenzhen dake lardin Guangdong, inda ya ganewa idanunsu manyan nasarori da ci gaban da birnin Shenzhen ya samu, musamman bayan da gwamnatin kasar Sin ta fara aiwatar da manufar yin gyare-gyare a gida, da bude kofa ga kasashen waje. Wakilinmu Murtala Zhang ya tattauna da mai martaba sarkin na Kano, ga cikakkiyar hirarsu.