in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Mutane 24 sun mutu sanadiyyar rikici a Jamhuriyar Afrika ta tsakiya
2017-08-11 10:23:03 cri
Rikicin da ya barke kwanaki biyu da suka gabata a garin Batangafo na Jamhuriyar Afrika ta Tsakiya, ya yi sanadin mutuwar mutane 24 tare da raunata wasu 17.

Rahoton kungiyar likitocin na gari na kowa MSF da ya bayyana adadin a jiya, ya ce bangarori na ci gaba da nuna adawa da wasu kungiyoyi masu dauke da makamai.

Tun bayan hambarar da Francois Bozize a watan Maris din 2013 da kawancen kungiyar 'yan tawaye ta Seleka ta yi, da kuma matsin lamba daga kasashen ketare, kasa da shekara guda bayan nan, kasar Afrika ta Tsakiya ta tsunduma cikin rikici, duk da kafa sabbin tsare-tsaren demokradiyya da aka yi, ciki har da lashe zaben shugaban kasa da Faustin-Archange Touadera ya yi cikin watan Fabrerun bara a Bangui. (Fa'iza Mustapha)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China