in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Jakadan Sin dake Nijeriya ya gana da sarkin Kano
2017-08-10 09:32:54 cri

Jakadan kasar Sin a Nijeriya Zhou Pingjian ya gana da Mai Martaba Sarkin Kano Muhammadu Sanusi na biyu a ranar Talata da ta gabata, inda suka tattauna kan yadda za a karfafa mu'amala tsakanin al'ummomin kasashen biyu, tare da habaka hadin gwiwar dake tsakanin kasashen yadda ya kamata.

Bisa gayyatar da Kungiyar sada zumunta tsakanin al'ummar kasar Sin da sauran kasashen duniya wato CPAFFC ta yi masa, Mai Martaba Sarkin Kano Muhammadu Sanusi na biyu, zai kawo ziyara kasar Sin daga yau 10 ga wata, zuwa ranar 17 ga watan nan da muke ciki, inda zai ziyarci biranen da su ka hada da Guangzhou da Shenzhen da Shanghai da kuma Beijing.

Mahaifin Muhammadu Sanusi na biyu, shi ne jakadan Nijeriya na farko a kasar Sin, tun bayan kulla huldar diflomasiyya tsakanin kasar Sin da Nijeriya a shekarar 1971. (Maryam)

Labarai masu Nasaba
ga wasu
v Sarkin Kano na shirin kawo ziyara kasar Sin 2017-08-09 19:32:39
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China