170809-xizang-amina.m4a
|
Kwanan baya, masana biyar daga ofishi mai kula da al'adu na yankin Xizang wato Tibet, yanki mai cin gashin kansa na Sin, sun kai ziyara a Abuja hedkwatar kasar Nigeria, don aiwatar da bikin kara fahimtar juna tsakanin kasashen biyu a fannin al'adu. Yayin bikin, masu fasaha na Nigeria sun dandana ganyen shayi da madara irin na kabilar Zang, sun koyi fasahar dab'i irin na Zang da ganewa idonsu rubutun kalmomin kabilar Zang da dai sauran al'adun kabilar Zang. Wani masanin zane-zane daga dakin nune-nunen abubuwan fasaha na Nigeria Simput Semshak, ya halarci wannan biki. Wakiliyarmu da ke Nigeria Amina ta yi hira da shi, ya bayyana yadda ya kalli wannan biki, kuma ya bayyana ra'ayinsa game da hadin gwiwa tsakanin kasashen Sin da Nigeria a wannan fanni.(Amina)