A cikin sakon, shugaba Xi ya ce, yana dora muhimmanci a kan dangantakar dake tsakanin kasashen biyu, kana zai kara kokari don ganin ya karfafa dangantakar abokantaka dake tsakanin Sin da kasar Rwanda, ta yadda za su kara cimma nasarori wadanda za su dace da muradun kasashe da ma al'ummominsu,da kuma daga matsayin hadin gwiwar kasashen biyu.
A ranar Asabar din da ta gabata ce aka sake zabar Kagame da babban rinjaye a zaben shugaban kasar da aka yi. (Ibrahim)