in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Ghana na shirin kafa doka wadda za ta takaita gibin kasafin kudi
2017-08-08 10:02:36 cri
Babban ministan mai lura da harkokin tattalin arziki a Ghana Yaw Osafo Maafo, ya ce kasarsa na shirin kafa wata doka, wadda za ta tabbatar da cewa ana kiyaye gibin dake tsakanin kasafin kudin kasar na kowace shekara, da mizanin awon karfin tattalin arzikin kasar ko GDP zuwa kaso 5 bisa dari.

Mr. Maafo wanda ya bayyana hakan, yayin wani dandalin tattaunawa game da tattalin arzikin kasar da ya gudana jiya Litinin, ya ce dokar za ta kunshi hukunci ga jami'an gwamnati da suka sabawa tanadinta.

Ministan ya kara da cewa, dokar na da nufin ceto kasar Ghana daga matsaloli masu alaka da bunkasar tattalin arziki. (Saminu Hassan)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China