Uwar gida Habitat ta ce ko alama gwamnati ba za ta kyale al'umma su ci gaba da gallazawa jami'an tsaro ba, duba da cewa a wasu lokutan hakan kan kai ga kisa ko garkuwa da jami'an tsaro, musamman ma jami'an hukumar kare hadurra ta kasar FRSC.
Ta ce dorewar hakan na iya zama barazana ga ayyukan jami'an tsaro, musamman ganin yadda a watan Yulin da ya gabata kadai, aka samu aukuwar irin wadannan hare hare har sau 10, ciki hadda harbin wasu jami'an hukumar ta FRSC da wasu 'yan sanda masu tsaron lafiyar kakakin majalisun dokokin jihar Abia suka yi a birnin Aba. (Saminu Hassan)