in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Gwamnan jihar Bauchi: fatara da rashin ilimi ne suka haifar da kalubalen tsaro a Nijeriya
2017-08-08 09:03:27 cri
Gwamnan jihar Bauchi dake arewa maso gabashin Nijeriya Mohammed Abubakar, ya alakanta matsalolin tsaro da suka addabi yankin arewacin kasar da rashin ilimi da fatara.

Gwamnan ya shaidawa karamar ministar kasafi da tsare-tsare Zainab Ahmed dake ziyara a jihar cewa, matsananciyar fatara da rashin ilimi ya sa matasa da dama shiga kungiyoyin 'yan ta'adda dake jefa al'umma cikin mawuyacin hali, musamman a yankin arewa maso gabas.

Abubakar Mohammed wanda ya bayyana haka a jiya, ya ce muddin ba a dauki matakin magance batutuwan ba, matsalar za ta ci gaba da ta'azzara.

Game da 'yan gudun hijira dake samun mafaka a jihar yanzu haka, Gwamnan ya ce jihar ba ta da sansanonin 'yan gudun hijira na din-din-din.

Har ila yau, gwamnan ya fadawa ministar cewa, yanzu 'yan gudun hijira na samun mafaka ne a wajen al'umma.

Ya kuma yabawa gwamnatin tarayyar kasar bisa taimakon kayayyakin jin kai da ta ba 'yan gudun hijirar dake jihar. (Fa'iza Mustapha)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China