in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Isra'ila za ta rufe rassan kafar yada labarai ta Al-Jazeera dake kasar
2017-08-07 10:20:44 cri
Ministan sadarwa na Isra'ila Ayoub Kara, ya sanar da shirinsa na rufe ofisoshin kafar yada labarai ta Al-Jazeera dake kasar, bayan firaministan kasar Benjamin Netanyahu ya zargi gidan talabijin din na Qatar da ingiza rikici.

Sai dai ya ce ba zai yiwu a rufe nan take ba, domin dole sai an dauki wasu matakan doka kafin aiwatar da shirin.

Ayoub Kara ya bayyana yayin wani taron manema labarai a jiya cewa, yana da niyyar ya bukaci ofishin watsa labarai na gwamnati, wato ofishin dake da alhakin bada katin izinin watsa labarai, ya kwace lasisin wakilan Al-Jazeera dake Isra'ila.

Ministan ya ce ya tuntubi kamfanonin dake nuna tashoshin talabijin na tauroron dan Adam, kuma ya bukaci su cire Al-jazeera daga cikin jerin tashoshinsu.

Ayoub Kara ya ce ya yanke shawarar daukar mataki a kan Al-Jazeera ne, saboda goyon bayan ta'addanci da take yi.

Ya kuma zargi Al-Jazeerar da rura wutar rikici da ya kai ga asarar rayukan 'yan kasar, yana mai bada misali da harin da aka kai ranar 14 ga watan Yulin da ya gabata a wajen harabar masallacin Al-Aqsa dake gabashin birnin Jerusalam, al'amarin da ya yi sanadin mutuwar 'yan sanda biyu. (Fa'iza Mustapha)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China