Dangane da halin da ake ciki a zirin Koriya a baya bayan nan, a yau Alhamis a nan Beijing, ministan harkokin wajen kasar Sin Wang Yi ya bayyana cewa, harkar tsaro, muhimmin batu ne mai nasaba da zirin Koriya. Mr. Wang ya ce kasar Sin na fatan cewa, sassan masu ruwa da tsaki za su tattauna cikin adalci, a kokarin lalubo bakin zaren hanyar daidaita kulawar da ake nuna wa juna ta fuskar tsaro, ta yadda za a tabbatar da rashin makaman nukiliya a zirin na Koriya. (Tasallah Yuan)