in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Rukunin farko na maniyyatan aikin hajjin bana na kasar Sin sun isa Saudiyya
2017-07-31 13:18:30 cri
Maniyyata 284 daga lardin Yunnan dake kudu maso yammacin kasar Sin, sun isa filin saukar jiragen sama na birnin Madina dake kasar Saudiyya a daren jiya Lahadi, wanda hakan ke nuna cewa, an fara jigilar maniyyatan kasar Sin masu aikin hajjin bana zuwa kasa mai tsarki.

Maniyyatan kasar Sin sama da dubu 12 ne za su gudanar da aikin hajjin bana a kasa mai tsarki wato Makka, wadanda za su tashi daga biranen Beijing, da Urumqi, da Lanzhou, da Yinchuan, da Xining, da Kunming. Da farko, za su yi ziyara da sauran ayyukan ibada a birnin Madina a tsawon kwanaki biyar, sa'an nan za su tashi zuwa Makka don sauke farali.

Kungiyar mabiya addinin Islama ta kasar Sin, ta zabo ma'aikata sama da sittin, wadanda za su samar da hidimomi daban-daban ga maniyyatan aikin hajjin na bana, wadanda suka kunshi ayyukan ibada, da kiwon lafiya, da tsaro, da abinci da gidajen kwana da sauransu, ta yadda maniyyatan za su sauke faralinsu lami lafiya kuma ba tare da fuskantar wata matsala ba.(Murtala Zhang)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China