Robert Mugabe, Ya yi kira da a kauracewa rikicin zabe domin ya na haifar da rashin sahihancin.
Ya ce yayin da ake shirin zabukan 2018, ya na mai bukatar al'ummar kasar su ci gaba da zama tsintsiya madaurinki daya wajen dabbaka zaman lafiya, inda ya ce kada a baiwa masu suka damar illata tsarin dimokaradiyyar su ba..
Har ila yau, shugaban ya ce ya na da yakinin 'yan sanda za su iya aikin da ya dace na tabbatar da zaman lafiya da doka da oda. (Fa'iza Mustapha)