in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
MDD ta yi Allah wadai da kashe jami'an wanzar da zaman lafiya a CAR
2017-07-27 11:20:33 cri
Sakatare janar na MDD Antonio Guterres, yayi Allah wadai da kisan jami'an MDDr biyu dake aikin wanzar da zaman lafiya a yankin kudu maso gabashin birnin Bangassou dake jamhuriyar tsakiyar Afrika CAR.

A ranar Talatar data gabata, aka hallaka biyu daga cikin jami'an wanzar da zaman lafiyar yan kasar Morocco, kana wani mutum guda kuma ya gamu da raunuka a lokacin wani hari da ake zargin magoya bayan kungiyar anti-Balaka suka kaddamar, kamar yadda MDD ta tabbatar da hakan. Al'amarin dai ya faru ne kwanaki biyu bayan wani makamancin harin da aka kaddamar kan jami'an wanzar da zaman lafiyar 'yan asalin kasar Morocco a birnin na Bangassou a ranar Lahadi, inda mutum guda ya rasa ransa.

Cikin wata sanarwa da aka fitar, Guterres ya bayyana cewa yayi matukar nuna damuwa dangane da tashin hankalin da ya barke a kudu maso gabashin jamhuriyar tsakiyar Afrika, lamarin da ke kara haifar da zaman tankiya sakamakon fadan kabilanci, wanda ke neman ta'azzara shirin zaman lafiya a kasar.

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China