in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Wakilin kasar Sin ya bayyana ra'ayoyin shugaban kasar a game da batun Palasdinu
2017-07-26 10:15:44 cri
A jiya Talata, kwamitin sulhun MDD ya kira taro game da batun Palasdinu, kuma zaunannen wakilin kasar Sin a MDD, Liu Jieyi, wanda shi ne shugaba karba karba na kwamitin a wannan wata, ya shugabanci taron, kuma mambobin kwamitin tare da wakilan kasashe da kungiyoyi kusan 50 da suka hada da Palasdinu da Isra'ila sun halarci taron.

Mr.Liu Jieyi ya bayyana ra'ayoyin da shugaban kasar Sin Xi Jinping ya gabatar a kwanan baya game da daidaita batun Palasdinu, wato na farko, a daidaita batun a siyasance bisa shirin "kasancewar kasashe biyu". Na biyu kuwa, a tsaya kan manufar hadin gwiwa da juna da samun tsaro mai dorewa. Na uku, a daidaita kokarin kasa da kasa, don kara hada karfin kasa da kasa a wajen wanzar da zaman lafiya a shiyyar. Sai kuma na hudu,

a wanzar da zaman lafiya ta hanyar samun ci gaban shiyyar.

Mr.Liu Jieyi ya ce, kasar Sin ta gabatar ra'ayoyin hudun ne bisa yanayin da ake ciki, kuma kokari ne da kasar ke yi game da daidaita batun Palasdinu, haka kuma manufa ce da kasar ke bi wajen daidaita batun a mataki na gaba.(Lubabatu)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China