Kwamishinan lafiya na jihar Lagos Jide Idris, ya ce cutar gudawa ta yi sanadin mutuwar mutane biyu daga cikin mutane 27 da suka kamu da ita a jihar dake a matsayin cibiyar kasuwanci ta kasar, a daidai lokacin da aka kara daura damarar takaita yaduwar cutar.
Yayin wani taron manema labarai da ya gudana a jiya, Jide Idris ya alakanta barkewar cutar da ambaliyar ruwa da aka fuskanta a wasu sassan jihar, biyo bayan mamakon ruwan sama da aka yi cikin 'yan kwanakin da suka wuce.
Kananan hukumomin da aka samu barkewar cutar sun hada da Shomolu da Oshodi-Isolo da kuma Surulere . (Fa'iza Mustapha)