Sakatare janar na MDD Antonio Guterres ya yi tir da kakkausar murya kan hare-haren kunar bakin wake da aka kai sansanoni biyu na 'yan gudun hijira a birnin Maidugurin jihar Borno dake arewa maso gabashin Nijeriya.
Harin da wasu mata 2 'yan kunar bakin wake suka kai ranar Litinin da ta gabata kan sansanonin 'yan gudun hijira dake kusa da birnin Maiduguri, ya yi sanadin mutuwar a kalla mutane 7 yayin da wasu 15 suka jikkata.
Wata sanarwa da aka fitar, ta ruwaito Antonio Guterres na yin kira da a hukunta wadanda ke da alhakin kai harin ta'addancin, inda ya jadadda goyon bayan MDD ga gwamnatin Nijeriya a yaki da take da ayyukan ta'addanci da tsatsauran ra'ayi. (Fa'iza Mustapha)