in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Shugaban Palasdinu ya jaddada kin yarda da kafa matsugunan Yahudawa
2017-07-14 11:06:40 cri
Yayin da shugaban Palasdinu Mahmoud Abbas ke zantawa da wakili na musamman na shugaban Amurka a fannin shawarwari na kasa da kasa, Mista Jason Greenblatt, a birnin Ramallah dake yammacin gabar kogin Jordan a jiya Alhamis, Abbas ya jaddada cewa, Palasdinu na adawa da matakin Isra'ila na gina matsugunan Yahudawa, gami da sauran wasu aikace-aikacen da za su iya kawo tsaiko, ga aiwatar da shirin "kasancewar kasashe biyu".

Abbas ya ce, gina matsugunan Yahudawa da Isra'ila ke yi, tare kuma da dokar da majalisar dokokin Isra'ila ta zartas wadda ita ce ta bada izinin kafa matsugunan Yahudawa a yammacin gabar kogin Jordan, dukkansu sun kawo illa ga kokarin da shugaban Amurka Donald Trump ya yi na farfado da zaman lafiya tsakanin Palasdinu da Isra'ila.

A nasa bangare sakatare-janar na kwamitin zartaswa na kungiyar 'yantar da Palasdinawa Saeb Erekat, ya fidda wata sanarwa a shekaran jiya, inda ya ce Palasdinu na fatan Amurka za ta iya tsara wani shiri, na kawo karshen mamayar da Isra'ila ta yi, da kafa wata 'yantacciyar kasar Palasdinu mai hedkwata a gabashin Kudus.(Murtala Zhang)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China