in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Mataimakin shugaban kasar Sin ya gana da takwaransa na kasar Equatorial Guinea
2017-07-13 16:20:35 cri
Mataimakin shugaban kasar Sin Li Yuanchao, ya yi shawarwari tare da takwaransa na kasar Equatorial Guinea, Mista Teodoro Nguema Obiang Mangue yau Alhamis a birnin Beijing na kasar Sin.

Li ya ce, akwai dadadden zumunci tsakanin kasar Sin da Equatorial Guinea. Yana fatan kasashen biyu za su kara samun fahimtar juna ta fuskar siyasa, da karfafa hadin-gwiwa, da mu'amala a fannonin da suka shafi zuba jari, da ayyukan gona, da harkokin yawon shakatawa, da al'adu da sauransu.

A nasa bangaren, Mista Mangue ya ce, kasarsa wato Equatorial Guinea na maida kasar Sin a matsayin wata kyakkyawar aminiya, kuma yana fatan dangantakar kasashen biyu za ta ci gaba da inganta a nan gaba.(Murtala Zhang)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China