in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Sudan na fatan Amurka za ta soke takunkumin da ta aza mata
2017-07-12 16:04:29 cri
Kwamishina mai kula da harkokin bada tallafin jin-kai na gwamnatin kasar Sudan, Ahmed Mohamed Adam ya fidda wata sanarwa jiya Talata, inda yake fatan gwamnatin Amurka za ta cika alkawarin da ta dauka, na sokewa Sudan takunkumi har abada.

A cewar Mohamed Adam, gwamnatin Sudan ta cika sharuddan da Amurka ta gindaya domin soke mata takunkumi, kuma an bude kashi 90 bisa dari na duk fadin yankin Sudan ga kungiyoyin kasa da kasa a halin yanzu.

Adam ya kuma ce, Sudan ta yi matukar kokari musamman ta fannin nuna jin-kai, ciki har da kai agajin jin-kai wuraren da suke fama da fadace-fadace, da saukaka ayyukan jin-kai, ta yadda ma'aikata masu samar da agajin za su isa yankunan dake fama da tashe-tashen hankali yadda ya kamata.(Murtala Zhang)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China