in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Ambaliyar ruwa ta yi sanadin mutuwar mutane 11 a Nijeriya
2017-07-11 09:57:15 cri
Hukumar bada agajin gaggawa ta jihar Niger dake arewa maso tsakiyar Nijeriya, ta tabbatar da mutuwar mutane 11 sanadiyar ambaliyar ruwa da ta auku a jihar ranar Lahadin da ta gabata.

Shugaban hukumar Ibrahim Inga ya bayyana a jiya cewa, daga cikin mutane 11 da suka mutu, gawarwakin mutane 8 kawai aka gano.

Ibrahim Inga ya shaidawa manema labarai cewa, ambaliyar ta lalata gidaje 90, kuma a kalla mutane 500 ne ta raba da gidajensu.

Ya ce gwamnati na shirya sansanonin wucin gadi domin tsugunar da wadanda suka rasa matsugunansu.

Ambaliyar dai ta shafi galibin mutanen da suka gina gidajen a kusa da bakin kogi a Suleja,yankin da ake samun hada-hadar jama'a sosai.

Makonni 6 da suka wuce, hukumar kula da yanayi ta kasar, ta mika gargadin aukuwar ambaliya a Lagos, da sauran biranen dake kusa da teku da ma wasu jihohi a fadin kasar dake yammacin Afrika. (Fa'iza Mustapha)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China