in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Shugaba Xi Jinping ya ja hankalin kungiyar BRICS game da daukar matakan bunkasa tattalin arzikin duniya bai daya
2017-07-07 19:17:16 cri

Xi Jinping wanda ya jagoranci kwarya kwaryar taron, ya kuma bayyana bukatar kara azama tsakanin kasashe mambobin kungiyar BRICS, a fannin warware dukkanin sabani da ake fuskanta tsakanin sassa daban daban na duniya cikin lumana, yana mai cewa akwai bukatar amfani da inuwar kungiyar G20, wajen karfafa hadin gwiwar tattalin arziki tsakanin sassa daban daban.

A na su bangaren, shugabanni mahalarta taron sun sha alwashin hada kai da juna, wajen ganin an cimma sakamako mai inganci, a taron kungiyar ta BRICS dake tafe nan gaba cikin wannan shekara, wanda kuma aka tsara gudanarwa a birnin Xiamen dake kudu maso gabashin kasar Sin.(Saminu Alhassan)


1  2  
Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China