in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Kasar Sin na sa ran taron G20 zai cimma matsaya guda kan cikinki cikin 'yanci
2017-07-07 09:48:03 cri
Mataimakin ministan harkokin kudin Kasar Sin Zhu Guangyao, ya ce kasarsa na sa ran taron kungiyar kasashe masu karfin tattalin arziki ta G20 da za a kaddamar yau Jumma'a a birnin Hamburg dake arewacin Jamus, zai cimma matsaya guda kan batun ciniki cikin 'yanci.

Da yake ganawa da manema labarai, Zhu ya ce taron na da matukar muhimmanci ga mambobi su tabbatar da tsara harkokin kudi da na tattalin arzikin kasashensu da inganta amfani da dabarun kula da hada-hadar takardar kudade ta yadda za su rike darajarsu da kula da harkokin kudaden shiga da wanda suke kashewa tare da tabbatar da sauye-sauye don samun dorewar ci gaban tattalin arzikin duniya.

Ya ce a matsayin kasar Sin na mai goyon bayan bunkasar tattalin arzikin duniya, ta hannun shawarar "ziri daya da hanya daya" da karfafa hadin kai ta yadda za a samar da makoma mai kyau ga dukkan bil'adama, a shirye take ta yi aiki da bangarori daban-daban na fadin duniya don samar da moriya ga al'ummar duniya.

Ya ce a fannin harkokin kudi kuwa, ma'aikatar kudi da babban bankin Jamus sun gabatar da wasu batutuwa uku da suka hada da karfafa tattalin arziki da inganta harkokin zuba jari musammam a nahiyar Afrika da kuma zamanantar da harkokin tattalin arziki, wandanda batutuwa ne da aka tattauna kansu yayin taron bara da ya gudana a Hangzhou, inda suka samu goyon bayan kasar Sin da sauran kasashe mambobin kungiyar G20. (Fa'iza Mustapha)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China