Kakakin ma'aikatar harkokin wajen kasar Sin Geng Shuang, ya bayyana cewa, tun fil azal, yankin Sikkim mallakar kasar Sin ne.
Mr. Geng ya bayyana hakan ne a Alhamis din nan. Ya ce ainihin dalilin da ya sa ministan tsaron kasar Indiya ke cewa bai kamata kasar Sin ta shiga cikin yankunan kasar Bhutan ba, yana so ne ya musunta keta ikon mallakar yankunan kasar Sin da dakarun Indiya suka yi, bisa hujjar wai suna kare kasar Bhutan. (Kande Gao)