Wannan rundunar sojoji sun kasance a wurin dake kusa da wani kauye a yankin Tassara dake yammacin kasar Nijer, inda suka gudanar da ayyukan hana fasa kwaurin miyagun kwayoyi.
A safiyar ranar 5 ga wata, wasu dakaru sun kai hari a sansanin rundunar.
An ruwaito hukumar tsaron kasar ta Nijer na cewa, dakarun sun gudu kuma sun yi awon gaba da motocin soji guda hudu. A halin yanzu, gwamnatin kasar ta dukufa don kama wadannan dakarun.
A ranar 16 ga wata, shugaban kasar Nijer Mahamadou Issoufou ya sanar da tsawaita dokar ta bace na tsawon watanni 3 a lardin Diffa dake kudancin kasar da kuma wasu larduna 6 dake yammacin kasar, domin fuskantar kalubalolin ta'addanci. (Maryam)