in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Kwamitin sulhun MDD ya yaba da gudummawar tawagar wanzar da zaman lafiya a Cote D'ivoire
2017-07-01 11:28:08 cri
Kwamitin tsaron Majalisar Dinkin Duniya ya fitar da wata sanarwa jiya Jumma'a, inda ya yabawa tawagar wanzar da zaman lafiya da MDD ta tura zuwa kasar Cote D'ivoire, saboda gagarumar gudummawar da ta bayar cikin shekaru 13 da suka shige, kana ya bukaci gwamnatin kasar da ta gaggauta yin garambawul ga hukumomin tsaro na kasar.

Sanarwar ta ce, kwamitin sulhun MDD ya nuna yabo ga babban ci gaban da kasar ta Cote D'ivoire ta samu, musamman ta fuskokin tabbatar da zaman lafiya da kwanciyar hankali gami da habaka tattalin arzikin kasar. Tawagar wanzar da zaman lafiya ta MDD ta kammala aikinta a ranar 30 ga watan Yuni, wadda ta bayar da gudummawa sosai wajen tabbatar da zaman lafiya da kwanciyar hankali da neman ci gaba a kasar ta Cote D'ivoire.

Har wa yau, sanarwar ta ce, bayan da tawagar wanzar da zaman lafiya ta MDD ta kammala aiki, ya kamata Cote D'ivoire ta ci gaba da kokari a fannoni daban-daban, ciki har da yanke hukunci ga wadanda suka aikata laifi, da neman samun sulhu tsakanin al'ummomin kasar, da yin garambawul ga hukumomin tsaro, da kuma kara baiwa mata ikon shiga fagen siyasa.(Murtala Zhang)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China