in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Gwamnatin kasar Sin ta dauki matakan hana kananan hukumomin kasar fadawa rikicin bashi
2017-06-28 19:44:30 cri
Gwamnatin kasar Sin ta bullo da tsarin da kananan hukumomin kasar za su rika bi wajen karbar bashi, a wani mataki na ganin an sarrafa kudade kamar yadda doka ta tanada.

Wani jami'in ofishin kididdigar kudade ta kasar (NAO) ne ya bayyana hakan,yana mai cewa, irin wadannan matakai sun hada da tsarin kason kudaden tsakanin kananan hukumomin, da yadda ake aiwatar da kasasfin kudi, magance matsalar kudi, da inganta matakan sanya ido.

Bayanai na nuna cewa, a 'yan shekarun nan, mahukunatan kasar Sin sun dauki kwararan matakai na magance fadawa hadarin basussuka. Baya ga yadda gwamnatin ta karfafa matakan bunkasa tattalin arzikin kasar. (Ibrahim)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China