in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Shugabannin kasa da kasa sun isa birnin Dalian domin halartar taron Davos
2017-06-27 11:16:21 cri
Kwanan baya, shugabannin kasa da kasa da suka hada da firaministan kasar Sweden Stefan Lofven, da kuma firaministan kasar Finland Juha Sipila da dai sauransu, sun isa birnin Dalian na kasar Sin domin halartar taron Davos na lokacin zafi na shekarar 2017.

A yau kuma Talata 27 ga wata, aka bude taron na Davos na lokacin zafi, a babbar cibiyar taron kasa da kasa ta birnin Dalian, kuma za a kammala taron a ranar 29 ga wata.

Wakilai kimanin dubu 2 wadanda suka zo daga kasashe sama da 80, na halartar taron na wannan karo, wanda aka yiwa take da "bunkasuwar da aka samu bisa fahimtar juna, a yayin babbar kwaskwarimar masana'antu karo na hudu", inda za a yi tarurukan tattaunawa sama da 200, kan harkokin dake shafar yadda za a fuskanci kalubalolin dake duniya, da kyautata tsarin kasa da kasa da dai sauransu. (Maryam)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China