170626karamar-salla-2017.m4a
|
Yau Litinin ranar 26 ga wata ne, musulmai a sassa daban-daban na duniya ciki har da na kasar Sin suka yi bikin karamar sallah bayan sha kwanaki 30 suna azumin watan Ramadan. Wakiliyarmu Fa'iza Mustapha ta je masallacin titin Niujie dake nan birnin Beijing don bikin karamar sallah. Titin Niujie dai wata babbar unguwar musulmai ce a nan birnin Beijing. A yau musulmai da suka je masallacin na Niujie ya zarce dubu dari daya. Ga rahoton da Fa'iza ta aiko mana daga msallacin Titin Niujie kan yadda musulmai suka yi bikin karamar sallah ta bana.