Hedkwatar aikin ceto ta kudu masu yammancin lardin ta sanar da cewa, da misalin karfe 10 na dare agogon yankin masu aikin ceto sun tono gawawwakin mutane 15.
Mista Gutteres ya jinjinawa tawagar jami'an bada agaji na kasar, kana ya ce MDD a shirye take ta ba da dukkan taimakon da hukumomin kasar Sin ke bukata.
An shafe dare guda ana cigaban da aikin ceton, inda dubban masu aikin ceto ke cigaba da gudanar da ayyukansu a yankin ta hanyar amfani da na'urorin hangen karkashin kasa da karnuka masu iya sansano abubuwan dake binne a karakshin kasa. Sai dai alamu na baya bayan nan na nuna cewa ba su gano alamun akwai abu mai sauran numfashi a karkashin kasa ba.
Babban sakataren ya aike da sakon ta'aziyya ga al'umma kasar da gwamnatin Sin bisa hasarar rayuka da aka samu, kana ya yi fatan samun sauki ga wadanda suka samu raunuka.(Ahmad Fagam)