in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Yara miliyan 5.6 ne ke cikin hadarin kamuwa da cuttutuka da ake samu daga ruwa a yankin tafkin Chadi
2017-06-24 12:59:02 cri
Asusun kula da kananan yara na MDD UNICEF, ya yi gargadin cewa, a lokacin da aka shiga yanayi na damina, sama da yara miliyan 5.6 ne ke cikin hadarin kamuwa da cututtukan da ake dauka daga ruwa kamar amai da gudawa, a yankunan tafkin Chadi dake fama da rikici.

Daraktan shirin bada agajin gaggawa na Asusun Manuel Fontaine, ya bayyana a jiya cewa, barazanar barkewar cututtukan a kasashen Kamaru da Chadi da Niger da Najeriya, na zuwa ne a daidai lokacin da ake kara fuskantar rashin tsaro da karin zirga-zirgar jama'a, musamman a yankin arewa maso gabashin Najeriya, yayin da kuma ambaliyar ruwa da rashin kyawun titi, zai yi gagarumin tasiri wajen rage isar kayayyakin jin kai zuwa wurare masu nisa.

Manuel Fontaine ya kara da cewa, UNICEF da sauran hukumomin abokan huldarsa, na aiki a yankin na tafkin Chadi, a wuraren da ke fuskantar hadarin barkewar cutar amai da gudawa, inda suke ilmantar da iyalai illolin dake tattare da cutar da kuma matakan da za su iya bi na kare kawunansu.

Duk da rashin kudi, jami'in ya ce UNICEF a bana, ya kuduri niyyar samarwa mutane miliyan 2.7 da tsafatataccen ruwa da suke bukata don rayuwa. (Fa'iza Mustapha)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China