in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Masar ta kara tsawaita dokar ta baci da watanni 3
2017-06-23 10:48:54 cri

Gwamnatin Masar ta yanke shawarar tsawaita dokar ta baci da ta sanya a kasar da watanni uku.

Jaridar Ahram ta kasar ta ruwaito cewa, gwamnatin ta yanke shawarar ne yayin taron majalisar zartarwar kasar da ya gudana jiya.

A ranar 11 ga watan Afrilun da ya gabata ne, majalisar dokokin kasar ta amince da matakin fadar shugaban kasar na sanya dokar ta baci na watnni uku a kasar, biyo bayan hare-hare bam da aka kai kan wata mujami'a, da suka yi sanadin mutuwar mutane 44.

A nata bangaren, ma'aikatar harkokin cikin gidan kasar ta sanar a jiya Alhamis cewa, sojoji sun kashe mutane 7 dake da alaka da hare-haren dake nuna adawa da kiristoci.

Ma'aikatar ta kara da cewa, sai da 'yan ta'addan da suka buya a yankin Assuit mai tsaunuka, suka yi musayar wuta da sojojin kafin a kashe su.

Tun bayan hambarar da Mohammed Morsi a shekarar 2013 ne kasar Masar ke fama da hare-haren ta'addanci. (Fa'zia Mustapha)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China