in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Kasashe duniya sun yaba ma kasar Sin kan inganta hadin gwiwar kasa da kasa don magance kwararar hamada
2017-06-21 15:12:45 cri
A jiya ne a birnin New York na Amurka zaunannen wakilin Sin dake MDD Liu Jieyi da takwaransa na kasar Kenya Macharia Kamau suka shugabanci taro na musamman game da batun magance kwararowar hamada a matsayin shugabannin rukunin abokan huldar kasa da kasa game da kiyaye muhalli.

Liu Jieyi ya bayyana cewa, Sin tana fatan kasashen duniya za su kara yin mu'amala da juna kan fasahohin magance kwararowar hamada, da sa kaimi ga yin hadin gwiwa a wannan fannin, da hada kai tare don samun ci gaba ba tare da gurbata yanayi ba, da gina duniya mai tsabta da kyaun gani.

Wakilan kasashen Afirka ta Kudu, Iran, Tunisia da Senegal da sauransu dake MDD sun yaba ma kasar Sin kan kokarinta na inganta hadin gwiwar kasa da kasa a fannin magance kwararowar hamada. Sun kuma yi nuni da cewa, Sin ta taimakawa kasashe masu tasowa wajen inganta karfinsu na magance kwararowar hamada da raya matakan samar da hatsi, da kyautata yanayi da muhallin halittu. (Zainab)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China