in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Jami'ai biyu na ofishin jakadanci na Pakistan a Afghanistan sun bace
2017-06-19 10:51:38 cri
A jiya Lahadi, ma'aikatar harkokin waje ta Pakistan ta bayyana cewa, jami'ai biyu na ofishin jakadancin kasar a Afghanistan sun bace a kan hanyarsu ta komawa Pakistan.

A wannan rana, kakakin ma'aikatar harkokin wajen Pakistan ya bayyana a cikin wata sanarwa cewa, bayan bacewar jami'an biyu, Pakistan ta yi mu'amala da Afghanistan nan take, inda ta bukaci Afghanistan din da ta ceto su, kuma ta tabbatar ta yi iyakacin kokarinta domin cafke wadanda suka aikata wannan danyen aiki. Sanarwar ta ce, Afghanistan ta riga ta kafa kwamitin bincike mai zaman kansa kan batun.

Tun da farko, kafofin yada labarai na Pakistan sun ba da labari cewa, wadannan jami'ai biyu sun yi aiki a karamin ofishin jakadancin Pakistan a birnin Jalalabad na Afghanistan. A ranar Jumma'a 16 ga wata, sun bace a kan hanyarsu ta komawa kasar Pakistan, ba su isa Torkham cikin lokaci ba.

Jakadan Afghanistan a Pakistan Omar Zakhilwal ya tabbatar da wannan batu.

Kawo yanzu babu wata kungiyar da ta shelanta daukar alhakin bacewar tasu.(Fatima)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China