Shugaban kungiyar wasan kwallon kwando ta Najeriya Musa Kida ya bayyana a jiya Lahadi cewa, zai bullo da sabbin manufofin da za su bunkasa wasan a lokacin shugabancinsa.
Kida dai ya yi nasarar zama shugaban kungiyar ta NBBF ce, a zaben hukumar wasannin da aka gudanar a ranar 13 ga watan Yunin wannan shekara a Abuja, babban birnin kasar.
Ya kuma bayyana aniyyar sabbin jagororin kungiyar ta ciyar da wasan kwallon kwando gaba a kasar.(Ibrahim)