Kakakin ma'aikatar harkokin wajen kasar Sin Lu Kang ya bayyana a yau Alhamis cewa, Mataimakin shugaban kasar Ghana Mahamudu Bawumia zai kawo ziyarar aiki a nan kasar Sin daga ranar 20 zuwa 25 ga watan Yunin da muke ciki bisa gayyatar takwaransa na kasar Sin Li Yuanchao.(Ibrahim)