Uganda: Mutanen da suka yi fasa kwaurin hauren giwa ba jami'an kasar Sin ba ne
Ma'aikatar harkokin wajen kasar Uganda ta sanar a kwanakin baya cewa, wasu mutanen da ake zarginsu da keta dokar kasar ta hanyar fasa kwaurin hauren giwa, ba jami'an diplomasiyya na kasar Sin ba ne. Dangane da wannan sanarwar, kakakin ma'aikatar harkokin wajen kasar Sin Lu Kang ya furta a yau Laraba cewa, kasar Sin ta yaba kan yadda gwamnatin kasar Uganda ta bayyana hakikanin abin da ya faru, har ma ta jaddada bukatar kyautata huldar dake tsakanin kasashen 2.(Bello Wang)
Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku