in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Kungiyar ILO ta yi kira da daidaita batun yaran dake aiki
2017-06-13 13:38:25 cri
Babban darektan kungiyar kwadago ta duniya (ILO) Guy Ryder ya yi kira ga kasashen duniya da su dauki matakai cikin gaggawa, domin daidaita batun kananan yaran dake aiki a yankunan dake fama da rikice-rikice da bala'u.

Ranar 12 ga watan Yuni, rana ce ta yaki da sanya yara kanana ayyuka ta duniya. A cikin sanarwar da ya fitar, mista Ryder ya yi kira ga kowa da kowa a duniya da ya mai da hankali kan tasirin da rikice-rikice da bala'u suka haifarwa yara da ake sakawa aiki. Ya jaddada cewa, dole ne kasa da kasa su dauki matakai cikin gaggawa, domin daidaita wannan batu.

A wannan rana kuma, kungiyar FAO ta MDD ta ba da sanarwar cewa, baki daya an samu yara miliyan 168 dake aiki a fadin duniya, a ciki yara sama da miliyan 98 suna aikin gona. Baya rashin biyansu albashi, har ma suna fuskantar hadurra iri iri. An ba da shaida cewa, a yayin da suke aikin gona, yawan yara da matasa da suka mutu da wadanda suka ji rauni ya dara na baligai. (Fatima)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China