in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Shugaban babban taron MDD ya yabawa matakan da kasar Sin ke dauka na tinkarar matsalar harkokin teku
2017-06-09 20:41:34 cri
Yayin da yake zantawa da manema labarai a jiya Alhamis, shugaban babban taro karo na 71, na Majalisar Dinkin Duniya, Mista Peter Thomsen, ya nuna babban yabo ga matakan da gwamnatin kasar Sin ke dauka, wajen tinkarar matsalolin da suka shafi harkokin teku. Ya kuma yi kira ga kasashe daban-daban da su karfafa ayyukan kare ruwan teku daga fannoni da dama.

Mista Thomsen ya ce, gwamnatin kasar Sin na nuna himma da kwazo, wajen shawo kan matsalar gurbacewar ruwan teku a halin yanzu, da kyautata wasu matakan da take dauka ta fuskar teku, lamarin da ya burge shi kwarai da gaske.

An gudanar da babban taro kan harkokin teku karo na farko na MDD a birnin New York a wannan mako, da zummar tabbatar da cimma daya daga cikin muhimman buri, na shirin neman ci gaba mai dorewa nan da shekara ta 2030, wato kiyayewa, gami da yin amfani da albarkatun ruwan teku cikin tsawon lokaci, ta yadda za'a samu ci gaba mai dorewa a harkokin tekun. (Murtala Zhang)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China