in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Guterres ya bukaci kasashen yankin gabas ta tsakiya da su guji tayar da hankali
2017-06-09 10:40:18 cri
Babban sakataren MDD Antonio Guterres ya yi kira ga kasashen yankin gabas ta tsakiya da su guji duk wani abin da zai kawo tashin hankali a yankin. Kalaman na Guterres na zuwa ne bayan da kasar Saudiya da kawayenta suka katse huldar diflomasiya da kasar Qatar a ranar Litinin.

Wata sanarwa da babban sakataren na MDD ya fitar ta hannun kakakinsa, ta bayyana cewa, ya damu matuka da abubuwan da ya lura suna faruwa a yankin gabas ta tsakiya.

Don haka ya bukaci kasashen da ke yankin, da su kare aukuwar duk wani tashin hankali, su kuma yi kokarin warware bambance-bambancen dake tsakaninsu, ta hanyar amfani da matakai na diflomasiya. Yana mai bayyana kudurinsa na goyon bayan irin wannan mataki a duk lokacin da bangarorin suka bukaci hakan.

Rahotanni na cewa, kasashen Saudiya da hadaddiyar daular Larabawa da Bahrai da Masar da Yemen da Maldives, duk sun yanke shawarar katse huldar diflomasiya da kasar ta Qatar ce, bisa zarginta da hada baki da kasar Iran wajen maraba kungiyoyin 'yan ta'adda baya.(Ibrahim)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China